ZAWIYOYI DA GUDUNMAWARSU WAJEN ILMANTARWA DA INGANTA RAYUWAR AL’UMMA

 

 ZAWIYOYI DA GUDUNMAWARSU WAJEN ILMANTARWA DA INGANTA RAYUWAR AL’UMMA

Tahir Lawan Muaz Attijaneey

dlmuaz.ara@buk.edu.ng

Gabatarwa:

Da sunan Allah mai rahama mai jinkai, tsaira da amincin Allah su tabbata ga shugaban talikai sayyadina Rasulillahi dan Abdukllahi da Aminatu, tare da Ahlin gidansa tsarkaka da Sahabbansa baki daya.

Bayan haka wannan maudu’I da aka bani nayi bayani akansa karkashin wannan mu’asasah ta AL-SUFF FOUNDATION yana da matukar fadi, hasali ma idan muka daukeshi gaba gaba zamuga ya kunshi bangarori biyu manya wato bayani kan zawiya sai kuma gudunmawarsu wajen ilmantarwa da inganta rayuwa, har ila yau idan muka koma zamuga cewa shin ana so ne ayi bayani akan tarihin hakan ko kuma ana so ne a kalli yadda yakamata zawiyoyi su zama a wannan zamani na karni na 21? Duk wadannan da ma wasu abubuwa na sanya abun ya zamo da fadi, amma saboda rashin lokaci mai tsawo da kuma kasancewata bana iya yawaita rubutun typing naga na takaita abin na bishi da audios da zasu karfafi gabobin sda zan tattauna su.

Saboda haka na raba bayanina izuwa nukdodi kamar haka:

1.  Maanar zawiya

2.  Takaitaccen bayanin kan tarihin zawiya a musulinci

3.  Gudunmawar da zawiyoyin darikun sufaye suka bayar na:

a.   Ilmantarwa

b.   Jihadi

c.   Kyautata tsarin zamantakewa

4.  Zawiyoyi a yau ina mafita?

5.  Cikawa.

1.  Maanar zawiya a lugga da isdilahi

Kalmar Zawiya a harshen Larabci an samo ta ne daga tushen  (ز و ى)  jam’insa shine zawiyat da zawaya, maanarsa shine gefe nako loko na wani bigire., daga wanna maana aka samo suna zawiya na isdilahi ta yadda mutane suka zamo suna ware loko a cikin gidajensu don su rika sallah ko karatun Alkur’ani da wirdai, an rawaito daya daga makarantar Alkur’ani da ake kira Abubakr bn Iyyashin kuma aka fi sani da SHU’UBAH daya ne daga marawaita Alkur’ani daga makaranta 7, almajirin Asimu, sadda zai rasu sai yar uwarsa ta fashe da kuka sai ya kalleta yace meye yasa zaki kuka? Ki duba waccan zawiyar (yai nuni da lokon da yake karanta Alkurani ) dan uwank yayi saukar Alkur’ani dubu 18 a cikinta.

Daga haka sai ma’anar ta koma tsakanin sufaye da suka zamo suna kebewa don bauta a wani wuri musamman masallatai dab a na jumaa ba suke kiransa ZAWIYA, shiyasa sai ya zamo lafazin ya shahara a hannunsu, har ila yau sufayen nan sun zamo masu sadaukantar da kansu ne wajen koyar da al’umma addininsu da kuma aiki da ilmin a zahiri da badini, sannan idan jihadi ya tashi zasu mike su amsa kira daga zawiyoyi, wannan maanar ta karshe ta sanya ak sansu a wasu kasashe da sunan MARABIT ko Ribat, musamman a kasar Misra, amma galibi irin wadannan anfi gina su a gefen daular musulinci don zaman kare iyakoki, kamar yadda zamuga anan kasar Hausa Sheikh Muhammadu Bello y zauna a wurno don zaman ribadi, to sufaye kan amfani da wadannan RIBAT a matsayin wajen bauta da kare kasar musulinci. A wasu kasashen kuma ana kiran zawiyoyi da sunan KHANIQAH خانقاه musamman a kasashen Farisa wadda Kalmar ma ta kahanikah an samo ta ne daga Farisanci, su bambamcinsu da sauran shine asali an samar dasu ne a hanyoyin sarakuna don zuwa yaki da ayyukan daula domin sarki ya tsaya da jamaa don hutawa da cin abinci daga karshe suka zamo wurin aje mabukata da masu bauta zahidai. A wasu kasashen kuma ana kiransu TAKAYA ko TAKIYYAH التكية التكايا musamman a kasashen Turkey zamani daular Usmaniyya wato Ottoman Empire.

A takaice a iya cewa Zawiya a isdilahi wurine da aka tanadeshi domin zaman masu ibada da masu neman ilmi da mabukata da kuma ciyar dasu da kula matafiya masu wucewa wato عابر سبيل da masu jihadi da shiryasu domin kare daular musulinci.

Da wannan bayani zamu gane cewa zawiya wata mu’assasah ce ta addini da ilmi da take jawo mutane ta hanyar wuridi da zikirai na darikun sufye wajen wanke musu zukata da taimaka musu da kuma amfani dasu wajen kare musulinci, sannan bata tsaya nan bat a shiga cikin rayuwar al’umma da bada gudunmawa mabambata. 

2.  Takaitaccen Bayanin Kan Tarihin Zawiya A Musulinci

Yana da matukar wahala a iya cewa ga lokacin da Zawiyoyi suka fara a tarihin musulinci saboda abune daya taallaka da abubnuwa dadama kamar jihadi da bayyanar sufaye da shehunan su, shi kuma sufanci baya yiwuwa saida wajen bauta da zaman muridai, shi kuma sufanci ya zamo abune mai zaman kansa a musulinci daga karni na biyu.

Don haka ma iya cewa  a dunkule tarihin zawiyoyi ya fara ne a musulinci kamar yadda muka nunar tun farkon karni na biyu a cikin gidaje amma zawiya da tsarinta a matsayin muasassah mai tsari tsayayye to yayi jinkiri har wajejen karni na hudu zuwa na shida a kasashen Maghrib wato Algeria Tunisia Morocco da sauransu. Duk da cewa dukkan ayyukan zawiya anma yinsa tun karni na biyu a kasashen larabawa da farisa daMasar wanda daga baya kuma tsarinta yayi karfi a kasashen na Maghrib da mukai bayani.

Tsarin zawiya ya zamo yayi karfi ne musamman sabida alakar Sharifai musamman a magrib da yadda suka zamo mafaka ta wadanda ake muzgunawa a siyasance, har takai zawiyoyi suna shiga shaanin siyasa sui tasiri musamman a karnonin baya bayan nan, misali akan hajka shine zawiyar Sunusiya a Libya da Zawiyar Tijaniya ta Shehu Umarul Futy a kasashen Africa ta Yamma musamman Mali da Senegal da makotansu, kamar yadda zamu gani, hak iruin yadda aka kafa daular Idisiyya ta kakannin Shehu Tijani a Morocco karkashin tuta ta sufanci da sharifta.

3.  Gudunmawar da zawiyoyin darikun sufaye suka bayar na:

Na daya: Ilmantarwa:

Kamar yadda aka nuna a bya cewa Sufaye sun zamar da zawiya wajen kkarantarwarsu da koyarwarsu, wannan ya sanya dukkan zawiyoyi da aka sani a duniyar muslilnci suka zamu wurare ne na karantarwa da daukar koyarwar Annabi saw kasancewar sufaye masu kira zuwa ga Agyaran zuciya sun zamo sun fi maida hankali wajen gyara halaye da koya adabu na nafsu da alakarta da mahalicci, hakan baya yiwuwa ba tare da sanin ilmin shariah ba kamar yadda Imamul Juniad yake cewa ‘ilminmu wannan abin daurewa ne da Alkur’ani da sunna wanda ya zamo bashi da rabo cikinsu to baya tare da tafiyar mu’’ wannan ya sa suka dora muridai kan nemaqn ilmin Alkurani da sunna har ya zamo manyan masana na Hadisai suka rika fita ta karkashin wadannan zawiyoyi, kai har manyan wadanda ake cece kuce akansu cikin sufanci duniya ta shaida malamai ne misali anan shine Babban Sufin nan Mansurul Hallaj, wanda yayi karatu mai zurfi a wajen Junaid da Sahlu at Tusturi, da abul hasani Annuri, shi kansa Sahlu Tustury melamine na Sunna da aka cira masa hulka a fagen ilmin Hadisi da tafsiri, haka akwai malamai irins Ibn Khafif Ash shirazi wanda Imam Az Zahabi yake cewa shehi ne abin koyi kuma babban masanin fikhu, mafi girma daga wannan shine Imamul Ghazali wanda ya rayu a matsayin maraya a hannun wani sufi day a fara kula da tarbiyyarsu a zawiyarsa kuma munsan yadda ya zamo malami da duniya ba wai kawai ta musulinci ba har kasashen yamma sun zamo suna cira masa hula a fagen sani a fanoni daban daban.

Daga manyan zawiyoyi da da suka bada gudunmawa ta ilmi akwai zawiyar sayyidi Abdulwahab Ash-shaarani a cikin karni na 10, wadda Alkali Muhyiddin yai masa wakafinta da kula da mazauna ciki tsawon rayuwarsu sarakuna da masu kudi suka rika bata kudi don tarbiya da koyar da addinin Allah, dubban muridai suka rika kwarara suna kwasar ilmi na sufanci da sharia, hakan ya basu dammar yin karatu mai zurfi da fidda masana, sun zamo suna kwana karatun Alkurani da koyar dashi da har mai littafin Tabakat ash shafi\iyyah yake cewamutane suna jin gunji kai kace gunjin kudan zumna saboda karatu a cikin ta dare da rana.

Bayan wannan ga majalisu na ilmi da aka tsara, da zarar mai koyar da ilmul hadith ya tashi mai tafsir zai zauna yana tashi mai sufanci zai zauna.

Zawiyar shehu Tijani rta a Fas ma ta ciri tuta wajen bada ilmi ya ishemu ishara yadda shehu yake zama ana jefo masa mas’aloli masu zurfi na ilmi yana warwarewa.

Haka idan muka zo nan zamuga yadda zawiyar Shehu Ibrahim ta zamo cibiyar ilmi daidai da zamani haka kuma zawiyoyin Shehu Atiku da sheu Tijani Usman da shehu Mai hula suka zamo, wadanda suma an fitar dasu ne a kasan zawiyoyin Sheikh Malam Abubakar Mijinyawa da Shehu Malam Muhammadu Salga. Wadannan zawiyoyi sune suka zamo fitalar kasar Hausa a karni na 9 zuwa na 20.

Na biyu: Jihadi

Daga gudunmawar zawiyoyi a duniyar musulinci akwai jihadi, wanda shi kuma yana kasancewa wajen yada musulinci ko kuma kauda zalinci daga kan wadanda ake zalinta ko kuma nemawa kasashen yanci, a duk wadannan bangarori Z\awiyoyi sun bada gudunmawa mai girman gaske, zamu dauki kowanne bangare mu gani.

A bangaren jihadi don yada musulinci akwai jihadi na takobi dana ruwan sanyi, a bangaren jihadi da takobi sufaye da suke jkan ribadi sun zamona farko wajen amsa daawar jihadi a duniyar musulinci kuma sun tsaya sun kawar da dauloli na kafirci, don kada mui nisa bari na bada misdali da jihadi da akayi a Macina da kafuwar Daular Takwalo ta Sayyadi Umar Alfuty a shekarun 1852 zuwa 1864 inda sayyadi Umar ya zamo Khalifa na wannan Daula ta Tijjaniya bayan day a assasa zawiyarsa a yankin Futa Jallon a wajejen 1840, bayan nan a hankali ya sami karfi day a rika yada Musulinci da darikarsa ta taijjaniya har ya fara yakar Sarakunan yankinsa da suke bautawa gumaka, bayan ya kasance yana yada ilmai na shariah da yada musulinci a wani gari da ake kira Dankraye abubuwa da dama suka faru da suka sanya ya dau makami ya yaki sarakunan wanda said a adadin yakokinsa suka kai32 banda kananan da bai je bad a sun kai 50. Wanda ya fara yaka shine wani sarki mai suna Yumba Sakho wanda kafiri ne kuma da yaga alherai Shehu umar ya sanya gaba da neman korar sa daga yankin baki daya ko kuma ma yakarsa da kasheshi, daga nan said a ya shejkaru 12 yana jihadi dabude garuruwa na kafirai da mataimakansu yana yada addini har dai ya samu shahada a 1864 daidai da hijra ta 1280.

A bangaren jihadin rowan sanyi kuwa zamuga gudunmawar Dariku da Zawiyoyi ne suka kafa Musulinci a duk yankin Yammacin Africa, musamman a nan Nigeria inda duk kasar Hausa ta shiga Musulinci ta hannun zawiyoyin Dariku da shehunansu da malamansu suke kai kawo a yanki, misali manyan shehunan wangarawa da suka zo Kano suka musiuluntar da Sarakunan Kano da jamarsa koda yake kafin zuwansu akwai musulinci amma shima dai yazo ne ta hannun manyan masu daawa sufaye da suke zuwa daga Arewacin Africa wato Biladil Maghrib. Hakanan zamuga zuwan Sheikh Abdulkarim al Maghili da yadda ya kara karffar Musulinci a wannan yanki na kasar Hausa, da yadda suka kafa zawiyoyi da dama da syuka dora aikinsu har yau din nan.

 Ta fuskar kauda zalincin sarakuna zamuga yadda Shehu Usman dan fodio yayi wanda abune sananne ga kowa.

A karshen wannan nukda azn cike da nemawa kasashe yanci da zawiyoyi sukai, babban misali shine jihadin Sunusiya a Libya kamar yadda na fada a baya wadda zawiyar wannan darika suka tunkari turawan Italia da suka mamaye kasarsu, kisser Umar Mukhtar sananniya ce ga kowanew musulmi a fadin duniya wanda shima dan darikar Sunusiyyah ne da ya  jagorannci jihadi da turawa.

A banhgaren Tijjaniya zanm buga misali da gudunmawar Zawiyar Tijaniya wajen yakart turawan Faransa da suka mamaye kasar Algeria mahaifar Maulabna shehu Tijani rta. Jikansa Sayyadi Ahmad Ammar ya zamo jagora tare dad an uwansa sayyadi Muhammadul Bashir aka kama a 10 February 1869 aka kaisu France aka yi musu daurin talala.

Haka shima sayyadi Ben Omar wanda ya ziyarci Nigeria  tun kafin bayyanar faira kuma sunb hadu da Shehu Ibrahim (har suka dau hoto yana zaune Shehu na tsaye  a bayansa) shima ya zamo jagora na yakar Turawan faransa kuma shima an kamashi.   

Na uku: Kyautata tsarin zamantakewa:

Daga abinda zawiyoyin Sufaye suka maida hankali akansa sjhine samar da zamantakewa mai kyau, wannan nukdah tana da alaka data baya baki daya ko muce itace hadafin dukkan abinda ya gabata na ilmantarwa da jihadi da bada mazauni ga mabukata, don haka bazan tsawaita kanta ba. Zawiyoyi sun kasance wuri na daidaita al\umma da basu kariya. Daga inganta al’umma akwai samar da ayyuka ga muridai da al’umma, zamuga irin wannan a tsarin tafiyar zawiyoyi irin na sayyid Malik Si na Senegal, haka na zamuga yadda zawiyoyi suke da tsarin wurin saukar Muridai da wajen abinci dad akin girka abinci dad akin karatu da dakunan khalwa da dakunan Darwishai wato maaikatan zawiyah bandaki na wanka dana tsuguno.

4.  Zawiyoyi a yau ina mafita?

A karshe zamu rufe da tambayar dake cewa menene zawiyoyi yakamata suyi kuma menene gyudunmawarsu a wannan zamani na cigaba da kuma kere kere? Me yakamata zawiya tayi don taimakawa al’umma a rayuwarsu? Yaya zawiya ya kamata ta zamo a yanzu? Wadannan tambayoyi ne da muke bukatar doguwar tattaunawa akansu don lalubo hanyar mafita duba dayadda zawiyoyi yau suka takaita kan abu daya kawai wato Zikiri da Wirdi, tabbas wannan shine aikin zawiya na farko, amma dai sauran ma basu gaza shi ko su zamo sababi ne na jawo bayi zuwa hanyar Allah. Don haka bazan tattauna wannan ba kasancewarsa maudu’I mai zaman kansa amma bisa ishara fadin Imam Malik dayace “ba abinda zai gyara karshen al’ummar nan said a abinda farkonta ya gyaru” maana yanzu dole ne sai mun koma tsarin zawiyoyi na baya da suka zamo mahada ta Addini da koyarwa da siyasa da kuma kyautat rayuwar al’umma da haska musu hanya mai kyau sawa’un a addini ko a rayuwa ko a siyasa, amma hakan bazai yuwu ba sai jagororin zawiyoyi sun yarda da canjin zamani ta hanyar tallafar muridai da aljihunsu da jkokarinsu da hanyoyin sanayya (connections) da  suke dasua duniya da cikin gida. Idan muka dauki tsari irin na kungiyar sufayen nan na kasar Turkey wato HIZMET ta fethullah Gulen wanda sun nuna a fili sun dauko zamani da tsarin Zawiya ta zamani duk da munada wasu mulahazozi da muke ganin lallai yakamata da darikarmu ta Tijjaniya da take kula kwarai da bangaren rayuwa ta ruhi.

5.  Cikawa:

A karshe inaga Zawiyoyi sun bada gudunmawa mai girma a rayuwar al’umma tun daga zamanin yaduwar Sufanci zuwa yau din nan duk da koma baya da aka samu a bangaren gudunmawar da Zawiyoyi suke bayarwa a cikin rayuwar al’umma ta yau da kullum. Muna fata allah ya karemun da abinda muka gabatar baki daya.

Wassalam

Dan uwanku

Tahir Lawan Muaz Attijaneey

Comments

Popular posts from this blog

SALLAR TARAWIHI DA TAHAJJUDI DA YADDA AKE YINSU

من خواص أذكار الطريقة التجانية حزب البحر للإمام الشاذلي

TARIHIN WAFATIN ANNABI SAW 1 DAGA TAHIR LAWAN MUAZ ATTIJANEEY