Silsilolin Darikar Tijaniya a Nigeria: jiya da yau.

 



Silsilolin Darikar Tijaniya a Nigeria: jiaya da yau.

Da sunan Allah mai rahma mai jin kai.

Gabatarwa:

Alhamdulillahi, wassalatu wassalam ala rasulillah wa alihi wa sahbihi wasallam.

Bayan haka, dalilin da yasa nai wannan rubutu shine tunatar da yan uwana Tijanawa gameda wani sashi na tarihin Darikar Tijaniaya a kasar Hausa musamman nan arewacin Nigeria, ta fuskar bada labarin hanyoyin zuwan Tijaniya da silsiloli na wannan darika, saboda lokaci ya tura ana mantawa da wasu manyan malamai da suka fara kawo Tijaniya kasar da kuma baiwa wannan darika gudunmawa ta bangarori da dama, har takai in akai maganarsu sai kaga matasan mu duk basu sansu ba, har takai ma ana neman kaskanta lamarin wadannan silsiloli ko amfani da wasu don dakile wadancan na farko. Don haka naga yakamata a takaice na rubuta wannan rubutu don fadakarwa.

Silsila a addini:

Silsila a larabci tana nufin sarka mai awarwaro da ake hada hancin zobe da zobe ya tashi sarka dga nan sai aka aro Kalmar akabawa duuk wata hanyar da aka ciro wani zance ko lamari daga wani zuwa wani, wato mutanen da aka ciro abin ta hannunsu daga farko zuwa karshe. Silsila takan zamo mai tsayi ko gajeruwa wadda a ilmin hadisi idan an ciro ta silsila mai tsayi ana kiran hanyar Nāzil mai sauka, idan gajeruwa ce ace da hadisin ‘āliy wato madaukaki. Daga nan aka gane idan silsilata akwai mutum 5 ta wancan akwai mutun 8 to tawa tafi daraja a galibi, saboda kusancina da mai maganar yafi kusa daf da daf. Amma nau’in mazajen dake cikin kowace silsila ka iya bada gudunmawa wajen fifita hadisi kan wani koda kuwa wancan yanada gajertar mazaje.

Zuwan Tijaniya kasar Hausa:

Akwai sabani da kuma rashin tabbas cikin cewa ga sadda Tijaniya tazo Nigeria, wasu na ganin Sheikh Umar Al Futi shine ya kawo Tijaniya sa’adda yazo Arewacin kasar nan ya zauna a Borno ya karaso kasar Hausa yya zauna a sokoto tareda Shehu Muhammadu Bello, har ma takai ya auri yarsa bayan ya auri yar shehun Borno. Hakanan ya shigo Kano ya assasa zawiya a  cikin lungunan unguwar Koki. Wanann ya faru  a tsakani shekarun 1831 zuwa 1839 wato lokacin da Shehu Umar Al Futi ya zauna shekaru 7 zuwa 8 a kasar Hausa. Kuma shekaru 15 kacal da wafatin Shehu Tijani. A wannan lokaci ne Tijaniya ta shigo, Shehu Umar Futi yu yada ta har aka rika tunanin ma Shehu Muhammad Bello ya karbi Tijaniya ma.

Umar AL FUTI Omar Tall


A wata riwayar ana ganin Tijaniya ma tazo ta hannun wasu da ba’a san ko su waye ba, tun zamanin Sarkin Kano Ibrahim Dabo 1819-1846 saboda kamar yadda Babban Malami na Madabo yake fada cewa kakanninsu tun zamanin Dabo duk Mukaddamai ne na Tijaniya, wannan na nuna mai yiwuwa Tijaniya shigo tun kan zuwan Shehu Umar Futi.

Silsilar Tijaniya:

Silsilar Tijaniya itace hanyar da aka karbo Darikar daga hannun Shehu Tijani har tazo kanmu yau, kuma wadannan silsiloli sunada yawa amma akwai masu shuhura sosai, akwai wadanda suka kebanta da wasu garuruwa ko Shehunai gwargwadon Alakarsu da Almajiran Shehu Tijani, don haka zamuga Shehunan Nigeria silsilarsu ta fara ne da silsilar Shehu Umarul Futi kamar yadda zamu gani a bayanin wadannan hanyoyi, koda yake dai bamu sami silsilarsa day a bayar ba kai tsaye ga wani a Nigeria said a ta biyo ta hannun almajiransa kamar su Alfa Nuhu da yazo daga baya.

Silsilolin Tijaniya kafin zuwan Faidah:

Zan ambaci kadan daga silsiloin dana samu ana amfani dasu kafin zuwan faidhar Shehu Ibrahim Niasse. Saboda sunada yawa amma dai zan zabi wasu na kawo don misali.

Silsilar Umarul Futy (sanadi Hashimiyi)

Ana kiran wannan sanadi da Silsilatuz zahabi wato sanadi na zinare, Wannan silsila a iya cewa shine sanadin da yake a hannun malamai da shehunanmu kafin zuwan Faidah, domin kuwa shine sanadin Maulanamu Sheikh Muhd Salga, shi kuma daga Sheikh Alfa Hashim Al-Futy, shikuma daga Sheikh Saidul Futy shikuma daga Shehu Umarul Futy, Shikuma daga Shehu Muhammadul Ghali shikuma daga Maulan Abul Abbasi Ahmadu Tijani RTA shi kuma daga Shugaban kowa da kowa sayyadul wujudi Muhammadu saw.

Wannan sanadi ne Maulana Shehu Atiku ya wake shia kasidarsa mai suna: طرائق الوصول إلى حضرة الرسول

Malam Muhammadu Salga


Amma wannan ba shine sanadi na farko da Malam Salga yake dashi ba, domin kuwa yana da sanadinsa na farko daga shehinsa dake Dandalin Turawa mai suna Sharif Muhammad b. Sheikh, wanda shi kuma ya karba daga Mahaifinsa, shi kuma ya karba kai tsaye daga Shehu Tijani. Wannan sanadi koda ban samu wani da yake bada darika dashi ba amma dai sanadi ne madaukaki kwarai kasancewarsa shima tsakaninsa da shehu Tijani mutum biyu ne rak. Haka da wat salsalar ta hannun wani sharifin Morocco mai suna Sheikh Maula Abdurrahman wanda akace yazo Kano a wajejen karshen zamanin Sarki Abbas 1910, Sannan da wata silsilar daga Sharif Ujdud wanda shima an sani yazo kasar nan a zamanin Sarkin Kano Abbas din dai, kuma yai wafati a hanyar sa ta zuwa Katsina har yanzu Kabarinsa na nan a Garin Bichi.

Sanadin Sheikh Ben Omar

Wanann sanadi yana komawa kan Sayyadi Ali Tamasini ne shima kuma yazo da hanyoyi mabambamta, saboda shi Sayyadi Tamasini shine ya tarbiyyanci ko ya jagoranci yayan Shehu Tijani rta bayan ya kwasosu daga Fas zuwa Aina Maḍi, amma dai sanadinsa da nasan malamanmu suna yawan bayar dashi kafin zuwan faidha shine:

1.  Ben Omar (Ban Amar)

2.  Daga mahaifinsa sayyadi Muhammadul Kabir

3.   daga Mahaifinsa sayyadi Muhammadul Bashir

4.  Daga Al-Qutb al’abd Lawi,

5.  Daga Al-Qutb Ali At-Tamāsīni

6.  daga Shehu Tijani rta.

Shehu Ibrahim Niasse da Sheikh Ben Omar


Shi Sheikh Ban Amar yazo Kano ne a 17 Rabīʿ II 1368/16 February 1949. A hannunsa Shehunanmu suka karba, Ban Amar shine wanda Shehu Ibrahim ya dauki hoto dashi yana zaune shehu Ibrahim na tsaye a gefensa Sai kuma:

Sanadin Sheikh Alfa Nuhu

sanadi Na biyun kuma da yaake koma kan sheu Tamāsīni wanda shehu Atiku yayi ishara dashi ne a littafinsa alfaidil Hami’I, wanda Malaminsa  Sheikh Alfa Nuhu ya bashi wanda yafi kowanne sanadi karancin Mutane, wato daga:

1.  Alfa Nuhu daga

2.   Daga Sheikh Yusuf Baba

3.  Daga Ali Tamasini

4.  Daga Shehu Tijani rta.

Shi kuma Alfa Nuhu yazo Kano ne a wajejen hijra ta 1353 wato wajejen 1933 zuwa 1934. kuma Malaman Kano sun amfanu dashi kamar Malam Salga ya karbi Ismul aazam a hannunsa. Haka Shehu Atiku ya karbi izini mutlaq a hannunsa kuma yabashi asraru da wannan silsila da muka ambata. (Duba faidil hami’I shafi na 118-119) abin lura anan shine har yanzu ban sami wata silsila madaukakiyar sanadi sama da wannan ba saboda mutum biyu ne kawai tsakanin mai ita da shehu Tijani.

Sanadin Sheikh Ahmad Hamahullahu

Wannan sanadi daga Maulana Shehu Abubakar Mijinyawa yake, na sameshi da rubutun hannunsa mai albarka kamar haka cikin Izinin day a bawa Almajirinsa Alhaji Ibrahim Musa Gashash ta:

1.  S Abubakar Mijinyawa

2.  Daga Abdullahi Bin Jibril,

3.  Daga Sharif Hamr bin Ibrahim ash shanjidi,

4.  Daga Qutbin zamaninsa masanin Allah Sayyidi Ahmad Hamahullah,

5.  Daga Masanin Allah Sheikh Tahir Bū Taibah At Tilmisānī,

6.  Daga masanin Allah Abdul Wahhab Binil Ahmar Attaiziyu,

7.  Daga Maulana Shehu Tijani rta.

Wannan sisilar ta Mutanen yammacin Africa ce, akwai wata makamanciyarta data biyo takan sayyidi Muhammadul Hafiz Ash-shankiti, wanda ya fara yada Tijjaniya a Africa ta yamma.

Akwai wani sanadin na Shehu Usman Alami wanda ya zo Kano tun zamanin sarkin Kano Usman Dan Tsoho wajejen 1923 itama tana komawa Kan Shehu Sukairaj ne.

Sanadin Darikar Tijaniya bayan Zuwan Faidah:

Sanadin Shehu Ibrahim (sanadi sukairajiyyi)

Bayan bayyanar Faidar Maulana Shehu Ibrahim Niasse wanda zuwansa na farko Kano a wantan Yuni 1945 ta zamo wani lokaci ne na juyin juya hali a Tijaniya a duniya, Shehu yazo da sabbin tunani na cigaba bayan kasancewarsa sahibul faidah da Shehu Tijani yayi albishirin bayyanar ta. Shehu yazo da sabon sanadi da yake bi takan sayyadi Ahmad Sukairaj kuma malaman mu kaf suka karba ya zamo sanadi asasi da ake bawa kowa darika akansa.

Wannan sanadi ga yadda yake:

1.  Daga Shehu Ibrahim Niasse

2.  Shikuma daga Sheikh Ahmad Sukairaj Al-iayashi

3.  Daga masanin Allah Qutb Al-Abd Lawi

4.  Daga Qutb Ali Tamāsīnī

5.  Daga Shehu Tijani rta

Sheikh Sukairaj tareda sarakunan Makka


Wannan sanadi shine mutane sukafi sani, amma bayan sa akwai wasu da Shehu yazo dasu kamar sanadin shehu Abdullahi zuwa kan Muhammadul Alawi, mu bar wannan haka tunda hadafinmu shine marhalar kawai da kuma jagoranta Shehu Ibrahim Niasse.

ABIN LURA

Abinda yakamata mu fahimta daga wadannan salsaloli shine dukkansu suna komawa kan mai darika ne Shehu Tijani, amma a ciki zamuga wata tafi wata tsayi, sannan akwai guda daya da take bi ta hannun yayan Shehu Tijani wasu kuma ta hannun Almajiransa. Koda yake ban kawo wadda take tana kaiwa har kan sayyadi Muhammadul Habib ko Muhammadul Kabir ba saboda bamu cika amfani da ita ba a Nigeria.

ME YASA AKA SAMU KHILAFA BIYU: ALGERIA DA MOROCCO?

Abune sananne an haifi shehu Tijania a Aina Mai dake Jihar Agwat ta Algeria amma ya kafa zawiyarsa a garin Fas na Kasar Morocco, duk da a baya babu kasashen da ake kira Algeria ko Morocco saidai yankuna, kuma muna ganin Khalifofin Shehu Tijani a Algeria da Morocco wato Aina Mai da ake mata kirari da ASIMATUL TARIQAH TIJANIYA da kuma FAS inda Kabarin Shehu Tijani yake. Tambaya anan yaya aka samun khalifanci biyu ko ma uku? Domin kuwa akwai wata khilafar a garin Tamasina dake algeria, To ku biyo ni kuji yadda akai.

Kwashe iyalin S. Tijani bayan wafatinsa:

Kafin wafatin shehu Tijani ya bada wasiyyar cewa Khalifansa shine Sayyadi Aliyut Tamasini haka kuma yana umartarsa daya kwashe duk iyalinsa ya maidasu Aina Mai yana cewa “yayana babu yadda zai dace dasu sai Sahara. Bayan dogon ja in ja da Mutanen Fas da Sayydi Tamasini da Maula Sulaiman sarkin Fas Sayyadi Ali Tamasini ya dauke duk iyalin Shehu Tijani ya maidasu Aina Mai ya zamo banda Kabarin Shehu babu kowa a Fas sai Almajiransa da khalifofinsa na Fas. Wannan ya sanya sai dai yayan Shehu Tijani da jikokinsa suzo ziyara fas su fita kamar kowa, amma bayan yancin kan Morocco daga Faransa wani daga zuriar Shehu Tijani wajejen 1911 ya dawo ya zauna a Fas shine daga nan aka samu Khalifancin yayansa na biyu a Fas bayan Aina Maḍi dake Algeria.

A can kuma Algeria din Sayyadi Ali Tamasini shine ya zamo babban Khalifan da yake jagorantar rayuwar Tarbiya yayan shehu Tijani har yayi wafati, sannan har yau zuriarsa sune suke wannan Khalifanci, shiyasa suma suna ganin khalifanscu sama yake da kowanne, khalifansu na yanzu sunansa Sayyidi Muhammadul Id Attijaneey, sai dai tunda akwai zawiayr Yayan Shehu Tijani wadda sayyadi Muhammadul Habib ya zamo Khalifa na farko bayan dawo dasu Aina Madhi ya sanya wannan ta zamo khalifanci babba na Duniya kuma kowa yake kallonta a haka saboda yadda yayan shehu suka sha gwagwarmaya da Turawa da yaransu har takai an kashe babban dan Shehu Tijani wato Muhammadul Kabir, an kama Jikan Shehu S Ahmad Ammar an kaishi har Faransa aka tsare shi, sheikh Ben Amar ma haka aka kama shi bayan zuwansa Nigeria da wasu kasashen Africa a 1950s.

Wannan Khalifa na yanzu da yazo Nigeria wato Sayyadi Ali Bel Arabi jikane na Ahmad Ammar dan Sayyadi Muhammadul Habib dan Shehu Tijani.

A wanna gaba ne nake so na nunwa yan uwa Tijanwa cewa ba wani uzuri da zaisa wani Batijjane ya kokarin kaucewa Khalifanci wadannan yaya na Shehu Tijani, saboda yana da wata silsila a hannunsa ba tasu ba, haka kuskure ne babba, domin duk masu silsilar da take hannun kowane Batijjane ta biyo ta kansu ne ko takan sayyadi Ali Tamasini wanda shine Khalifan Shehu Tijani na farko, kuma ya zamo jagoran daya sanya yayan Shehu Tijani kan kafa Khilafa ta mahaifinsu da zata zamo uwa ga kowane Khalifa a Duniya.

Faiah babban reshen Tijaniya a yau:

Wannan nukda da nake son taunawa tanada matukar muhimmanci garemu Tijanawa musamman yan faira, saboda kasancewarmu munyi nasha nasha a cikin wannan Faira ne ya zamo bama hango cewa akwai Tijanawa wadanda bayan FAIRA ba, kuma bamu da labarin wasu shiyasa har in ance ga Tijanawa bay an faira ba sai kaga muna mamaki, to musani cewa tabbas yau babu wani reshe mafi girma a Tijaniya sama da Faiḍa Ibrahimiyya, saboda yadda jagoranta ya zamo gagara badau a duniyar sufanci da ilmi da wayewa, amma bayan faira akwai wasu bangarorin Tijaniya da suke bada gudunmawa wajen yada wannan darika, daga ciki akwai:

1.  Bangaren Sheikh Umarul Futy:

Bangarene babba da wata rana zamu ware lokaci mui Magana akansa daban, amma kamar yadda na fada shine ya yada darikar Tijaniya a Africa ta yamma fiye da kowa cikin karni na 19, ciki harda kasar Hausa, kuma mun kawo muku silsilarsa, kuam har yau akwai Tijaniya Umariya a duniya musamman a kasashen Mali da Guine da Senegal, a Nigeria ma akwaisu musamman a Elleman Tijani dake kasar Hadejia.

2.  Bangaren Haj Malik Sy:

Haj Malik Sy


Sheikh Malik Sy shehi ne na Tijaniya day a kafa bangarensa na Tijaniya an haifeshi a 1885 a arewacin Senegal ya rasu a 1922 a kuma har yanzu akwai mabiyansa masu tarin yawa a Senegal da makotanta haka yana da mabiya a kasashen ketare hard a Amurka wanda sunada foundation mai suna (Islamic Tijaniya Foundation of America ITFA).

3.  Tijaniya Hamawiyya:

Shi wannan bangare munyi bayani kan sisilarsa a baya wato mabiya Sheikh Ahmad Hamahullahu an haifeshi a wani gari da ake kira Tishit a gabashin Murtania wajejen 1882 Hamahullah waliyyine mai ban mamaki kuma yayi yaki da turawan faransa har takai sun kamashi sun daureshi a Faransa daga baya zuwa kasar Kwadebuwa wato Ivory cost har yanzu kuma suna da mabiya a kasashen Murtania da makotanta, shehu Atiku yana Tawassuli dashi a wata kasidarsa yana cewa:

بسيدي أحمد حماه الله ** سيدنا أحمد يا الله



Shima insah Allah wata rana zamu ware rubutu na musamman kan wannan Malami.

Wadannan sune mafi shahara cikin manyan bangarorin Tijaniya daba yan faira ba kuma silsilarsu take wanzuwa har yau har gobe.

Abinda ya rage mana mu sani tunda muna da bangarori to ya zamo mun san kowane bangare kuma mu girmama kowace nasaba kasancewarta nasab ceTijaniya, duk almajirai ne na Shehu Tijani kuma shi sukewa aiki. Shiyasa ma da aka tambayi Sheu Atiku gameda Tijanawa dab a yan faira ba sai yace Tijanawa ne amma sun rasa wani alheri mai yawa da ShehubIbrahim yazo dashi.

Ina ganin wannan bayanin da nayi ya ishemu ishara, amma dai zan jaddada kira na ga yan uwana Tijanawa mu san cewa Shehu Tijani ya zamo mana a matakin farko, kuma duk daga yadda ka fito ko daga salsalar Tijaniyarka take ka sani Shehu Tijani shine bango kuma baka neman izinin kowa wajen zuwa wajensa ko Khalifofinsa.

Allah ya datar damu

Dan uwanku

Tahir LAWAN Mu’az Attijaneey

Zangon bare bari Birnin Kano

Litinin 14 ga Jumada Sani 1443. 17 Junairu 2022

NB: Za’a ci gaba da gyara wannan makala gwargwadon yadda aka samu gyararrakin malamanmu.

 

Comments

Post a Comment

Popular posts from this blog

SALLAR TARAWIHI DA TAHAJJUDI DA YADDA AKE YINSU

من خواص أذكار الطريقة التجانية حزب البحر للإمام الشاذلي

TARIHIN WAFATIN ANNABI SAW 1 DAGA TAHIR LAWAN MUAZ ATTIJANEEY