ALMUNTAKIMU: daga Shehu Ibrahim Niasse




WASIKAR BARRANTA DA MASU KETA SHARIA DAGA MAULANMU SHEKH IBRAHIM INYASS AL KAULAKHI
Da sunnan Allah Mai rahama mai jinqai mai tsananin kamu mabuwayi wanda ya gagari kowa mai girma, tsira da aminci bias Manzo Shugaba bawa wanda yake cewa: “Ya Fadimatu bazan miki komai ba daga Ubangiji.”
   Bayan gode masa da abinda ya dace sallamata ta isa izuwa danmu AHMAD CIYAMU da MALIK SO izuwa ma duk wanda ya tsaya kan wannan takarda na daga wand yake da’awar nasabtuwa izuwa garemu, abinda wannan ke wajabtawa shine sanarwa da cewa mutum biyu basa tare dani kuma su bakomai bane acikin lamarin wannan Dariqa, Majzubi da baiyi suluki ba, da saliki da baiyi jazba ba in har suka wanzu akan halinsu, kuma suka tsaya ga barin tafiyarsu. Kuma ni sha’ani na kamar yadda kuka sani duk mai son ya kasance tare dani acikin hali to yabi hanyata a cikin zantuka da ayyuka ta hanyar bin umarni da nisantar abubuwan hanawa, a zahiri da badini da kuma kishirwa da shaukantuwa izuwa saduwa (WUSULI) da kuma yardarm da Allah da Manzonsa, Amma wanda yake jingina kansa damu kuma yake haikewa wani abu na savawa shari’a mai tsarki mai girma ta hanyar kutsawa abubuwan haramtawa da barin abubuwan umarni to ina shaidawa Allah ina shaida muku cewa ni na barranta dashi. Ya Allah babu ruwana da abinda wadannan mutane ke aikatawa “wadannan da suke savawa umarnin sa su tsautu kafin fitina ta samesu ko kuma azaba abar sawa radadi” “ku tuba izuwa ga Allah yaku muminai baki daya”.
    Abinda kuka fada kuma na cewa muridina jakace dake cike da asraru na halarori hakane, sai dai waye muridina daga cikinku? Shiyafi wahala daga jar zaiba a wurinku. Inko lamarin nan ya kasance kamar yadda kuka fada dinnan ne to ya kusata na dauke izni daga kan dukkan mukaddamin da ake kutsawa abubuwan haramtawa a halararsa kuma bai tsaya da abinda ya wajaba akansa ba, inko ya gaza to yaiyo hijra izuwa ga Allah da kuma Manzonsa da kuma garemu.   Kuma wallahi babu anbinda ya tsaida sairin wadannan mutane har suka koma suna izuwa debe kewa da fararru sai dai tsawon lokacin su da sukai batare damu ba, domin anan wurinmu akwai matasa kanana da suka mance dandanon sha’awa, kai takai acikinsu akwai wadanda ya mance matarsa bai zuwa mata saida izini da takurawa. Haka Dalibaina suke ba sabanin haka ba.
Komawa ga Allah dole ne da tuba da bin umarni da nisantar abun hani da gudun duniya da tsantseni da koyon ilmi. Allah (S.W.T) yana fadawa waliyyin waliyyai “kace ubangiji ka kara min ilmi.” Abinda ya dace da muridi karya tsaida (Sairinsa) tafiyarsa har sai ya risku dani kuma lamarinsa ya shige min duhu, to a sannan sai ya tafi ya nemi wani shehin da yafini daukaka a mukami.
    Ku sani Allah Yaji kanku-cewa da yawa da yawa daga masu da’awa suna toshe mutane daga tafarkin Allah ta hanyasr rashin istikama daidaituwarsu. Duk wanda ko ya danganta da Allah kuma ya zamo yana toshe mutane ga barin tafarkinsa to haka yayi fito-na-fito da Allah da yaki sai ya zamo yana cikin zurin masu inkari da tsiyacewa, saboda kasancewarsa sababine na haka (ga wasu). Don haka ba makawa gareku da ku halarcemu a mafi yawan lokuta don ku karbi ladubban (suluki) tafiya cikin Allah. Kamar yadda kuka karbi hakikar jazba. Wanda ya aikata haka to ya rabauta rabo mai girma.
Ba makawa gareku daga canja abubuwan ki da suke faruwa cikin yan uwa, da hannu da harshe da kuma zuciya kamar yadda yazo a hadisi.
    Kuma ba makawa ga duk mai son amfanuwa daya kiyaye abinda ke fitowa daga garemu na wasiyya a waka ko a zube. Wannan wasika kiyayeta wajibine ga dukkan maridi. Wanda ya tsaya akanta kuma ya kwafeta ya lazimceta ya karantata kullum.
     Ku tsaida sallah ka bada zakka ku azumci watan Ramadan ku hajjanci daki ga wanda ya sami ikon zuwa gareshi kuyi sadakar dukiya don zatin Allah ta’ala yazo acikin hadisin muslim daga manzon Allah (SAW) “tsarki yanki ne na imani Alhamdu lillalahi tan cika ma;auni (mizani) subhanallahi walhamdulillah tana cikawa ko ta cika abinda ke tsakanin sammai da kassai, sallah haske ce hakuri haskene, Alkur’ani hujja ce a gareka ko akanka mutane sune sammako akwai mai sayar da ransa ko mai yenta shi ko mai halakar dashi.”
   Allah (SWA) yana fada shine kuwa mafigaskiyar musu fada “hakika Allah yana umarni da adalci da kyautayi da bayarwa ga ma’abota kusaci yana kuma hani ga barin alfasha da abin ki da zalunci”
    Kaico dukkan kaico ga wanda baya fuskantar hukuncin Allah da manzonsa da karba cikakkiya. Sai dai wanda littafinan wannan ya sameshi ya tuba ya sauri ya riski abinda zai iya to wannan yana da arzikin duniya da lahira “Allah ya yafe abinda ya rigaya” amma wanda bai tsuatu ba to ma shaidawa Allah nima ina shaida cewa babu ni bashi. Banyi baram baram da mutun ba kuwa sai bayan da barrantar Allah da manzonsa dashi.
    Ina horonku da yawaita karanta salatil fatihi lima uglika. Ina kuma umartaku da boye sirrika a fadi da aikace. Ku kubar bayyanawa da zacen Alhalin hakiku, ku shiga hanyar madaidaiciya wannan abubawan sha’awa duk dagutu ne kuke bautamasa bayan kunyi da’awa Imani. Allah (S.W.T) Yana cewa: “wanda yakafircewa Dagutu yai Imani da Allah to haqiqa yayi riko da igiya mai karfi da bata tsinkewa Allah Mai jine masani.”
    Kai Ahmad Ciyam ka isar da wannan littafi ga duk mai dangantuwa damu ka aikawa kowane Babba a kowane wuri kwafi dan ya karantashi ga wadanda suke  tare dashi da wadanda  suke kewayensa.
    Ina fata daga Allah Yasa zukata masu haske su karvi wannan da kuma kunnuwa masu sauraro. Allah Ya shiryemu ya shiryeku.
                                                                                WASSALAM WANDA YARUBUTA
IBRAHIM DAN ALHAJI ABDULLAHI ALKAULAKHI ATTIJANI
 ALLAH YA KIYAYESHI YA KARESHI DAGA DUKKAN CUTA. AMIN.     

Comments

Popular posts from this blog

SALLAR TARAWIHI DA TAHAJJUDI DA YADDA AKE YINSU

من خواص أذكار الطريقة التجانية حزب البحر للإمام الشاذلي

TARIHIN WAFATIN ANNABI SAW 1 DAGA TAHIR LAWAN MUAZ ATTIJANEEY