WAFATIN ANNABI SAW (6)





SAYYADI ABUBAKAR YANA JAGORANTAR SALLAH:
Sa'adda rashin lafiyar Manzon (SAW) ta karu, fita ta gagara gareshi zuwa jan sallah sai yace "Ku umarci Ababakar yayi sallah da mutane". Sai Sayyada Aisha tace "Ya Annabin Allah Abubakar mutum ne mai tsaushin zuciya sai Annabi (SAW) ya sake cewa "ko umarci Ababakar yayi sallah da mutane", sai Aisha ya sake fadin abinda ta fada da farko sai yace "kudai'yan uwan Yusifa ne, nace ku umarci Abubakar yayi sallah da mutane, wato yana nufin sun cika jayayya kamar 'yan uwan Annabi Yusuf, ita kuma Aisha (RA) tana sone a janye jagorancin sallah daga mahafinta gudun kada mutane su fitunu da shi, kuma tasan mutane basu son duk wanda akace yau ya tsaya mahallin Manzo saw, amma Annabi (SAW) ya dage sai shi.
To daga nan Sayyadina Abubakar ya cigaba da jagorantar sallah har tsawon kwana hudu, wato zuwa ranar da Manzon Allah (SAW) yayi wafati, inda ya jagoranci salloli goma sha bakwai 17.
An rawaito daga Sayyada Aisha (RTA), cewa Manzon (SAW) ya shigo dakinta lokacin yana dafe da kafadar Fadlu da Sayyadi Ali (RTA) koda ya shiga sai ciwon ya rufeshi, sai yace "ku kwarara min ruwa salka bakwai daga rijiyoyi daban-daban".
Aisha tace sai muka zaunar dashi akan wata kwarya ta Sayyada Hafsat (RTA) muka kwarara masa wannan ruwa har sai da ya dinga dago mana hannu yana cewa (yaisa ya isa) daga nan sai yaji sauki, sai ya fito ya zauna a kan matattakalar minbari yace da mutane ku matso gareni, sai mutane suka taru sai yace "Allah ya la'anci Yahudawa da Nasara don sun riki kabarurrukan Annabawansu gumaken da ake bautawa.
A ranar Alhamis kafin wafati da kana 4 Manzon (SAW) yace da Sahabbansa ko kawo min takarda da alkalami in rubuta muku wani abu da bazaku bata ba a bayansa" a lokacin ciwo ya kama Manzon (SAW) sosai a cikin dakin kuma akwai mutane, daga cikinsu akwai Sayyada Umar dan Khaddab sai yace "ciwo ne yake rinjayarsa, kuma akwai Alkur'ani a wurinku littafin Allah ya isheku, to sai wadanda suke dakin sukayi sabani a tsakaninsu wasu na akawo wasu suna cewa a'a. koda jayayya ta yawata sai Manzon (SAW) yace ku tashi kubani wuri".
A wannan rana Manzon (SAW) yai wasiyya da cewa kada a bar Bayahude ko Nasara ko Mushriki a Jazirar Larabawa.
Manzon (SAW) ya zamo kafin yasa S. Abubakar sallah yana  fitowa sallah duk kuwa da irin tsananin ciwonsa, har sai da wannan rana tazo inda karshen sallarsa da mutane itace sallar magriba inda ya karanta suratul Mursalati. Bukhari ne ya rawaito daga ummil Fadli

Comments

Popular posts from this blog

SALLAR TARAWIHI DA TAHAJJUDI DA YADDA AKE YINSU

من خواص أذكار الطريقة التجانية حزب البحر للإمام الشاذلي

TARIHIN WAFATIN ANNABI SAW 1 DAGA TAHIR LAWAN MUAZ ATTIJANEEY