WAFATIN SHEHU IBRAHIM NIASSE DA ABUBUWAN DA YA BARI

بسم الله الرحمن الرحيم
الحمد لله رب العالمين، والصلاة والسلام على أشرف الأنبياء والمرسلين سيدنا محمد وعلى آله وصحابته والتابعين ومن تبعهم بإحسان إلى يوم الدين.

1.0. GABATARWA
Maulana Shehu Ibrahim Niasse ya rayu ne baki daya cikin Hidimtawa manzonAllah SAW da kuma kokarin Tarbiyyar Alumma kan Sunnarsa. Hakan ne yasa Shehu ya zamo hoto ne da kowa zai iya Kallo yai koyi dashi, kamar yadda saadda ya koma ga Allah ya bar abubuwa da daman gaske wadanda har yanzu ake ta sherhi akansu, don haka wannan makala zata kalli shin wai da Shehu yai wafati wadanne  abubuwa ne suka wanzu nasa.
1.1. WAFATIN SHEHU IBRAHIM
Maulana Shehu Ibrahim Niasse yayi rashin lafiya da ta sanya ya tafi jinya a wani Asibiti a Birnin London na kasar Birtaniya, wadanda suka sahibci Shehu A wannan Tafiya akwai babban Jikansa Sayyidi Imam Hasan Cisse wanda kuma ya zamo Khalifarsa. Sayyidi Hasan ya bada Labarin yadda ya dauki wani darasi a lokacin jinyar Shehu da yayi wanda yaga Lallai sai ya isar wa da duk Almajirin Maulana Shehu Ibrahim Niasse, wannan ba wani abu bane kuwa illa Tsaida Farillai dake Kansa na Sallah da kuma duk wani Wurdi nasa Shehu Bai fasa ba duk da radadin ciwo.
Daga wadanda suka je dubiya akwai Shehu Mahmood Salga shimaya bamu Labarin Yadda suka tarar da Maulana Shehu Ibrahim Niasse a cikin ciwo amma da lokacin Sallah yayi sai Shehu ya Miko Hannu a miko masa Dutse da zai shafa yai Taimama yasa sayyid Imam Hasan Cisse ya fuskantardashi Kibla saboda Taazzarar da yin Alwala da tashi yaiwa Shehu. A wannan gaba ne wani Malamin dan kasar Misra (Egypt) mai suna Sheikh MuhammadMahmood Sawwaf yake cewa cikin Hakkin Shehu
“Shehu Ibrahim Nyass shine babban Shehun wannan yanki bari shine yake tsayawa da karfinsa a gaban duk wani motsi na kungiyoyi masu kalubalantar musulunci…kuma mutane da dama Sun Musulunta a Hannunsa”
Maulana Shehu Ibrahim Niasse awananan Hali ya koma ga Allah Ranar 15 ga Rajab 1395. July 1975. Duk duniya ta gigiza da rashin wannan gwarzo da afirka ta jima bata ga kamarsa ba. Kuma aka dauko gawarsa mai girma zuwa Senegal aka binne shi a Madinarsa ta Kaulach.
1.2. ABUBUWAN DA MAULANA SHEHU IBRAHIM NIASSE YA BARI
 Maulana Shehu Ibrahim Niasse kamar Sauran waliyyai yai wafati yabar abubuwa da dama, wadanda bazamu iya ganesu baki daya ba amma zamu iya kallon abubuwannan ta fuska uku:
1. koyarwarsa a addini a aikace. 2. Koyarwasa a rubuce. 3. Zuriarsa da Almajiransa.
2.0. koyarwarsa a addini. Bazan tsawaita anan ba, tunda abinda Maulana Shehu Ibrahim Niasse yake maimaitawa dayane cewa a dabiantu da Sifofi na Annabi saw da koyi da sunnarsa, ya ishemu isharaabinda Malaminnan Na Misra ya fada akansa, kamar yadda aikin da Shehu yayi a lokacin Rashin Lafiyarsa ya ishemu Ishara don haka Shehu Ya yankewa kowa Hanzari cikin Riko da Adiini da Shariar Annabi saw ta hanyar aikatasu har numfashinsa na karshe, Shehu yana cewa cikin diwanin kan Manufarsa a addini:
وأمة قصدي فيهم أن أسوقهم**
 إلى حضرة البر الرحيم إلهنا
“Ni alumma manufata cikinsu na korasu zuwa Halarar Allah mai jin kai” hakana Shehu ya fadi awata hara da akai dashi a Hijaz (Saudiyya) cewa shi Manufofinsa a daawa sune:
Kiran wadanda ba Musulmi ba su shiiga addini
 Wayar da kan Musulmi har tafiyarsu a Allah ta dore su kara imani kan    wanda suke dashi
Yada Luggar Alkurani wato Larabci.
Zurfafa jin yan uwantaka ta Musulunci a zukatan Bayi
Taimakekeniya tare da kungiyoyin Musulunci na Duniya
Yakar yan Baranda Yan MUSHAN (missionaries) na Kiristanci da Yahudanci.
2.1 To anan sai mui duba tsakani mugani shin da shehu ya bar maa wannan abu bayan yai wafati kowa ya dora a inda Shehu ya bari ko kuwa an shga wasu abubuwa daban? Shi kuwaShehu daya zaga duniya ya yada addini cewa yayi yayi ne don mu yan baya mu dauki misali ya zamo mana sample ne kamar yadda yake cewa:
علوت البحار الزاخرات وإنني **
 علوت القرى والمدن بلح الجبالا
أروم رضى الباري لنصرة دينه **
وأبرز للجيل الجديد مـــــــــــــــــــــــــــــــثالا
2.2.  KOYARWAR SHEHU A RUBUCE
A gurguje ina nufi Talifan da ya bari, sashin masu binkice sun tabbatar da cewa Shehu ya rubuta abinda bai gaza Littafi 70 ba
Daga wadannan Littafai bari nai bayanin Biyu ko uku a takaice don muga irin abinda suka kunsa:
2.3.  RAF’UL MALAAM
shi wannan Littafi ya kunshi koyar da Sallah ne kamar yadda Manzon Allah SAW ya koyar da kafa hujjoji da hadisai ingattatu, kuma asali ance Shehu ya wallafa shi ne lokacin da aka samu sabani tsakanin Malamai a garin Kano kan Mas’alar (KABALU) har takai ana kafirta masu dora hannu a kirji in suna Sallah, kuma daga wannan littafi rigima ta kare.
2.4 TABSIRATUL ANAM FI ANNAL ILMA HUWAL IMAM
. Shehu ya wallafashi kan nusar da Musulmi cewa lallai fa Ilmi shine jagora, don haka ne ma muke kiran Littafin TAALIMIN SHEHU,  shehu ya kawo ayoyi da hadisai da labarai dake nuna dole kowane musulmi ya tashi ya nemi Ilmi.
2.5. SABILUSSALAM FI IBQA’IL MAQAM. Shehu ya wallafashi ne lokacin da mai fatawa na Saudi ya bada fatawa kan a cire maqam Ibrahim daga inda yake, shehu yace dole abarshi domin aikin Annabi saawda Sahabbai kamar s Umar ya tabbatar dashi anan. Wannan littafi na nuna bin kwakwkwafin Sunna da shehu yake dashi da kuma matsayinsa a duniyar musulunci wanda aka dawo akabi raayin shehu tilas.
2.6.NUJUMUL HUDA wannan littafi yazo ne airin wannan lokaci da muke ciki yanzu inda akesamun masu cin mutunci ko Tauye darajar Annabi saw, ance ansamu wani ne daya fifita wasu akan Manzin Allah saw, Maulana Shehu Ibrahim Niasseban wani jinkiri ba ya dau Alkalmi da takarda ya wallafa littafinnan don kare Darajar Annabi saw tare da nuna cewa babu wani mutum a gaban Annabi saw.
3.0. ZURI’AR SHEHU DA ALMAJIRANSA
3.1. Daga abun da Shehu ya bari yabar Zuria da dama da kuma Almajirai da ba san adadinsu ba.
Mun samu labari Shehu ya bar yaya sama da 70 wadanda akasarinsu Mahaddata Alqurani ne da Masu riko da Sunna. Daga ciki zan so na ambaci Khalifa Sayyidi Abdullahi Niasse da Sheikh Ahmad Tijani da Sheikh Muhammadun Nazeer Sayyidiu Maamoon Sayyidi Baba Lameen, wadanda duniya ta crawa Hula.
3.2. A mata koda Shehu bai haifi kowa ba sai Sayyidah Maryam to wannan ya isa, dalili kuwabayan ta haddace Alqurani tana da shekaru 15 afagen ilmi kuwa koda a mata na duniya da suke takama da yancin mata da cewa sun cimma wani abu to basu kere Sayyidah Maryam ba, saboda yadda ta dora kan hanyar Shehu cikin koyar da Alqurani ga dubban daruruwan yara tare da Larabci sannan in sun tasa a tura su kasashen waje don karo ilmi na addini dana zamani mai zurfi a kasashen Larabawa da Turawa. Kai takai matsayin da Sayyidah Maryam ta shiga alaqar diplomasiyya tsakanin Senegal da Iran lokacin da suka sami matsala kuma ta warware da taimakawar Sayyidah Maryam haka kuma Senegal da Sudan sun sami matsala har aka rufe embassy dinsu a Dakar da Khartoom, amma ta shiga tsakani ta gana da Shugaban Sudan AL BASHEER tasa aka bude musu embassy dinsu.
Haka ga mu muma anan Mun sami Sayyida Ummu Hanee wadda take jangorar Bayi kan hanyar mahaifinta a garin Kano dama nigeria baki daya>
3.3. Ta fuskar Almajirai zan maimaita abinda na fada wata muhadara ta a wannan dandaline na cewar wata Jaridar Murtaniya ta Kaddara Almajirai da mabiya Shehu da Miliyan Arba’in da shida.
3.4. koda shehu bai bar Almajirai ba akace ya bar Manyan da duniya ta jinjina musu irinsu Shehunan Kano Sanannu  S. Atiku Sanka S Tijjani Usman Shehu Mai Hula S Sani Kafinga da su sharif Ibrahim Saleh Wanda yau a fagen Hadsi baya da Tamka a duniya, ko irinsu Sheikh Barham Mahmood Job wanda ya zamo tamkar inuwa ne ga Shehu yana binsa ko ina kuma ya kwasa daga kwaranyensa ya zamo shugaban Kungiyar Malamai ta Afrika to ai ya ishemu ishara kuma sun ishemu Fitilar Haskawa cikin tafiyar mu a Allah.
Da wadannan Kalmomi nake cewea Allah kasa mu amfana da abinda Shehu Ya bari duniya da Lahira.
Wassalam Naku
Tahir Lawan Muaz Atijaneey
08060306021-08099475470
dlmuaz.ara@buk.edu.ng
Bourda

Comments

Popular posts from this blog

SALLAR TARAWIHI DA TAHAJJUDI DA YADDA AKE YINSU

من خواص أذكار الطريقة التجانية حزب البحر للإمام الشاذلي

TARIHIN WAFATIN ANNABI SAW 1 DAGA TAHIR LAWAN MUAZ ATTIJANEEY