WAFATIN ANNABI SAW (5)



MANZON YA FARA RASHIN LAFIYA:

Ya gabata garemu cewa sadda Manzon (SAW) ya dawo daga Hajji, sai yaji ciwon kai iri na matafiya bayan 'yan kwanaki ya warke, sai kuma cikin watan safar wajejen 29 – ko 28 ya fara rashin lafiyar da yayo wafati a cikinta.
A farkon rashin lafiyar sa Manzon (SAW) ya fara da ciwon kai, kuma ya zamo yana ciratuwa daga dakin waccan matar tasa, zuwa waccan, daga karshe rashin lafiyar sa tayi tsanani a dakin Maimunatu bintil Haris, sai ya tara matansa ya nemi izininsu kan yayi jiyyarsa a dakin S. Aisha (RTA). Sai suka yarda da Shugaban Adalai SAW.
MUTANEN MADINA AL-ANSAR DA TSORON RABUWARSU DA MANZON (SAW):
An rawaito sa'adda Manzon Allah (SAW) yake rashin lafiya har ya kasa fitowa sallah, sai mutan Madina wato Ansaru suka taru a cikin masallacin Manzon (SAW), suna masu tausayawa da kuma tsananin tsoron ace Annabi (SAW) ya bar duniya. Saboda haka Abbasu dan Abdulmuttalib (RA) ya shigo ya sanar da Manzon Allah (SAW) abinda suke ciki, nan take Annabi (SAW) ya fito kansa a sunkuye ya dafa S. Ali da Fadlu, Abbasu kuma a gabansa, har sai da ya isa bakin Minbarinsa ya zauna, sannan mutane suka zauna suka nutsu sai ya godewa Allah ya yabeshi, sannan yace "yaku mutane labari ya isar min cewa ku kuna tsoron mutuwar Annabinku, shin an wanzar da wani Annabi gabanin zuwana? Balle ni a wanzar dani a cikin ku? To kusani nifa mai haduwa ne da Ubangijina, haka kuma masu haduwane dani, saboda haka ina yi muku nasiha da muhajirai na farko da alheri…. Ina yi mumu nasiha da Ansaru da alheri domin sune wadanda suka tanadi gida da imani gareku, ku kyautata musu, ba sune suka raba yayan itacensu daku ba? Ba sune suka yalwata muku a cikin gidansu ba ba sune suka zabeku akansu ba?! suka baku abubuwansu koda suna da bukata?! Sai Sahabbai suka rushed a kuka, daganan mazon Allah (saw) ya koma gida.

Comments

Popular posts from this blog

SALLAR TARAWIHI DA TAHAJJUDI DA YADDA AKE YINSU

من خواص أذكار الطريقة التجانية حزب البحر للإمام الشاذلي

TARIHIN WAFATIN ANNABI SAW 1 DAGA TAHIR LAWAN MUAZ ATTIJANEEY